Ukraine na shirin samar da cibiyoyin hatsi a Najeriya | Yakinsu da Rasha Zai komo da Nigeria kenan?

 Gwamnatin Ukraine ta bayyana shirinta na samar da cibiyoyin hatsi a Najeriya da sauran kasashen Afirka yayin da ta ba Najeriya gudummawar kimanin tan 25,000 na hatsi domin bunkasa alakar kasashen biyu.

Ministan harkokin noma da abinci na Ukraine, Mykola Solskyi ne ya bayyana haka ranar Talata a Abuja lokacin da ya jagoranci tawagar da ta gana da ministan harkokin wajen kasar, Geoffrey Onyeama.

Solskyi ya ce hatsi daga Ukraine zai isa Najeriya a cikin watan Fabrairu a karkashin shirin da ta tsara.


Ya ce duk da ƴakin da kasar ke yi da Rasha, masana'antar abinci ta ƙasar na son kulla alaka da Najeriya, inda ya kara da cewa "muna matukar godiya a gare ku cewa kasar ku a shirye take ta bunkasa dangantakar".

Ministan ya ce haɓaka irin waɗannan wuraren zai ba da damar shigo da hatsi masu inganci a cikin Najeriya kuma hakan zai yi tasiri mai kyau kan farashin kayaki.

Post a Comment

Previous Post Next Post