Video - Sojoji sun ceto 'yan China bakwai daga 'yan Kidnapping

 Rundunar Sojan Sama ta Najeriya ta ce ta ceto 'yan ƙasar China bakwai da wasu 'yan bindiga suka yi garkuwa da su a yankin Birnin Gwari na Jihar Kaduna.

Shiga Nan 👇👇👇Domin Kallo Kaitsaye

Sanarwar da rundunar ta fitar ta ce dakarunta na Tawaga ta 271 ne suka ceto mutanen a yau Asabar.

An sace su ne a watan Yuni da ya gabata lokacin da suke tsaka da aiki a wurin haƙar ma'adanai da ke Ajata-Aboki na Ƙaramar Hukumar Shiroro a Jihar Neja.

Sanarwar ta ce 'yan bindigar sun yi ta kansu lokacin da suka ga dakarun tawagar mai mutum 35 tsakar dare a yankin Kanfani Doka da Gwaska, inda suka bar 'yan Chinan da suka kama da kuma makamansu.

An kai su asibitin sansanin soja don duba lafiyarsu a Kaduna.

"Na ji daɗi sosai da ƙoƙarin da sojojinmu na musamman suka yi a Birnin Gwari da sauran wurare kuma ina da ƙwarin gwiwar nan gaba kaɗan za mu kakkaɓe duk 'yan ta'addan da ke yankin," a cewar Babban Hafsan Sojan Sama na Najeriya Oladayo Amao.

Post a Comment

Previous Post Next Post